Tsohon Gwamnan Kano kuma jigo a jam'iyyar PDP Malam Ibrahim Shekarau ya ce ba shi da niyyar komawa jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya.

Shekarau na mayar da martani ne kan wasu rahotanni da ke cewa Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje na zawarcinsa zuwa APC.
A ranar Alhamis wasu kafafen yada labarai suka bayar da rahoton cewa jiga-jigan APC a Kano da Abuja sun fara tattaunawa da Malam Shekarau da nufin shawo kansa zuwa jam'iyyar.

Jaridar Daily Trust ta ce lamarin ya karfafa ne saboda sauya shekarar da Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso, wanda abokin hamayyar siyasar Shekarau ne, ya yi daga APC zuwa PDP.

Sai dai mai magana da yawun tsohon gwamnan Sule Ya'u Sule, ya shaida wa BBC cewa mutanen da jaridar ta ce sun gana da APC ba wakilansu ba ne, kuma ba da yawun tsohon gwamnan suka yi ba.

"Ya ce ba da hannun malam suka yi ba. Wadannan mutane ne da dama can sun raba-gari da Malam Shekarau," a cewar Sule Ya'u.

Ya kara da cewa ba su da "masaniyar" ganawar da aka ce Ganduje ya yi da wasu da ke ikirarin cewa su wakilan Shekarau ne.

Post a Comment

 
Top