Wani mutum ne yaje wajen cin abinci (Restaurant). Ya samu waje ya zauna sai ya kwalawa mai restaurant kira da karfi yace “hado min plate na N2000 kuma ki hadawa kowa dake wajen nan plate na N3000 saboda idan ina cin abinci, ina so naga kowa yana ci”.
Duk mutanen dake wajen suka fara godiya yayinda mai restaurant ta zubawa kowa nasa ta kawo masa. Bayan mutumin ya gama cin abinci sai ya kuma cewa mai abincin “kawo min drinks na N500 kuma ki kaiwa kowa na N1000 saboda idan ina
shan abu, ina so naga kowa yana sha”.

Post a Comment

 
Top