Mun dai samu cewa Rahma Sadau din ta yada labarin ne da jaridar nan ta Pulse Nigeriya Hausa ta wallafa mai taken 'Nafisa Abdullahi: Jaruma ta zama jkada' inda ta rubuta 'Congrats sis' a harshen turanci da ke nufin 'ina taya ki murna 'yar uwa' da Hausa.
A kwanan baya ne dai cikin watan Afrilu kungiyar mashirya fina finai na Kannywood suka shiga tsakanin jaruman yan fim din nan su biyu Nafisa Abdullahi da Hadiza Gabon bayan wata arkalla data shiga tsakaninsu.
Shaidan dai ya shiga tsakanin jarumai matan ne a jihar Kaduna yayin da suke bakin aiki wajen shirya wani fim a garin na Kaduna, kamar yadda jaridar Rariya ta ruwaito.
Post a Comment
Click to see the code!
To insert emoticon you must added at least one space before the code.