Hukumar yan sanda na jihar Katsina sun gabatar da wasu yan fashi da makami da suka kama gaban yan jarida ciki har da wasu dalibai guda biyu.

Abdulrasheed Ibrahimmai shekaru 20 dalibi ne wadda ke aji uku a makarantarKwara state College of Educationdake garinLafiagishi kuma Opeyemi Agbooladan shekara 19 dalibinKwara state Polytechnic.

Arewaswag.com ta samu kuma cewa dai hukumar yan sanda ta bayyana cewa Matasan suna cikin ƙungiyar yan fashi da makamin da aka kama kwannan baya a karamar hukumarBakori.

Ibrahim ya tabbatar ma manema labarai cewa an kama shi yayin da suke fashi shi kuma Agboola yace yan hukuma sun kama shi a teburin mai shayi yayin da yake jiran Ibrahim da sauran membobin ƙungiyar su.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar yan sanda dake jihar Katsina DSP Gambo Isaya tabbatar da laifin su kana har yanzu hukumar na cigaba da yin bincike.

Post a Comment

 
Top