Akan Korar Rahama tacce bazatace kome ba saide ta godewa dukkan masoyan da suka fito kwarsu da kwarkwata domin taimaka mata.

Akan zargin da akeyi mata kuwa Rahama tacce ita dai yar Arewace kuma bazataba Tubewa tsirarba domin tayi fim.
Image © Arewarmu

A Batun addini kuma tacce masu tsaurin addini su gane cewa fa Fim Fim ne, bawai yana nuna zuciyar mai yin wasan kokwayo ba.

Da aka tambayeta batun Nollywood da saban fim din da ta dauka mai suna Sons of the caliphate- Rahaman tacce tayi farin ciki mutuka da fim din wadda yadauki har tsawon sati 11 suna dauka, duk da cewar yan Arewa da yawa suna ganin cewa fim din wanni irin cin fuska ne domin ya nemi ya nuna yadda masu arzikin arewacin ke batanci.

Jarumar ta kara da cewa bawai tana son ta koma kudancin najeriya da aiki banne kawai tana so ta hada wasannin turanci da na hausa.

Da aka tambayeta ko tana da saurayi Rahama tacce A’a ita bata da wanni saurayi a duniya ita kawai yar yarinya ce yar shekara 23.

Post a Comment

 
Top