Ban Ji Dadin Sakin Bidiyon Ganduje Na Karbar Rashawa Da Aka Yi Ba, Saboda Cin Fuska Ne Ga Hausa/Fulani Da Arewa, Cewar Kwankwaso

"Na samu labarin bidiyon tun kafin su sake shi. Kuma na kira su na ce kar su sake shi. Saboda faifain bidiyon illa ne ga jihar Kano, Hausa Fulani, da 'yan Arewa da ma musilmin duniya.

Sun saki  shi bidiyon ne lokacin da muke rigimar fitar da Dan takarar Gwamna.

Nayi yaki da sakin bidiyon ne saboda ina da yakini cewa za mu ci zabe ko babu faifen vidiyon.

"Bana goyon bayan sakin faifen bidiyon, saboda ba iya Gwamna zai taba har da iyalinsa da kuma al'ummar Kano", cewar Sanata Kwankwaso a hirar sa da gidan radio Dala FM Radio Kano.

Post a Comment

 
Top