Gwamna Aminu Waziri Tambuwal  ya aikewa majalisar dokoki ta jaha da wasika inda ya gabatar da sunan Hon Manir Dan Iya a matsayin sabon mataimakin Gwamnan jahar Sokoto, kasancewa tsohon mataimakin gwamna Alh Ahmad Aliyu ya sauka daga mukamin nashi da kanshi .

Don haka kakakin majalisar Alh Salihu Mai Daji ya bada umurni a aikawa Alh Manir Daniya da wasikar gayyata domin  bayyana a zauren majalisar gobe alhamis idan Allah ya kaimu domin tantancewa.


Post a Comment

 
Top