Ya ce ya zama dole gwamnati ta koyi wasu darusa daga yadda kungiyar yan ta’addan Boko Haram ya fara.
Zakzaky dai na tsare tun a watan Disamban 2015, tun bayan wani karo da mabinsa suka yi da rundunar sojin Najeriya a Zaria, jihar Kaduna. An yi zargin cewa sama da mambobin kungiyar 350 ne suka mutu a wannan karo.
An ci gaba da tsare Zakzaky duk da umurnin da kotu ta bayar na a sake shi wanda ya kai ga yawan zanga-zanga da karo tsakanin hukumomin tsaro da mabiyansa.
Gumi ya shawarci gwamnatin tarayya da ta sake shi domin guje ma billowar wata kungiya ta ta’addanci.
Da yake ci gaba da Magana, malamin na musulunci ya ce ya zama dole gwamnati ta mutunta umurnin kotu ta yi umurni ga sakin sa.
A cewarsa Zakzaky ya fara gane ikon gwamnati, da zaran ta sake shi.
Post a Comment
Click to see the code!
To insert emoticon you must added at least one space before the code.