Wani mutum ya yi mutuwar gaggawa yayin da ya kafe a jikin wata katuwar mata yana jima'i da ita.

Wata Magosha wacce kalma ce da ake nufin Karuwa da yaren kasar Afrika ta kudu, ta shaida wa manema labarai cewa "wannan mutum yana cikin jima'i da ni, haka kurum na ga nan take ya fara shakewa, shakar iska ya gagare shi, daga bisani sai ya bingire".

Ta kara da cewa "Ni ban taba ganin irin wannan ba a rayuwata na saduwa da maza, amma bayan na gan ya bingire sai na sa hannu na dan ture shi daga jjkina zuwa daya bangaren gado, daga nan sai na je na shaida wa Manajan Otel da muke ciki, shi kuma ya zo da yansanda".

Karanta  Ababe da ke haddasa mutuwar na miji kan mace yayin jima'i da yadda za a kiyaye

Shi dai wannan mutum da ba'a san ko waye ba , ana kyautata zaton ya zo ne daga garin Tshepisong kusa da  Kagiso.

Kakakin yansanda na  Roodepoort Sergeant Juliet Mogale ta tabbatar da faruwar lamarin, hakazalika ta tabbatar da mutuwar mutumin, ta kuma ce yansanda sun fara gudaanar da bincike.

DAGA ISYAKU.COM

Copyright, do not copy and paste our news on your blog without express written permission from us.

Shiga shafin mu na Facebook facebook.com/isyakuweb

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0

Domin Flashin ko gyaran wayarka Garzaya zuwa SENIORA TECH,shago mai lamba 50, hawa na sama gefen hagu,TAUSHI PLAZA , yamma daga gidan marigayi Waziri Umaru,kan Tiltin Ahmadu Bello, Nassarawa, Birnin kebbi jihar Kebbi. Barka da zuwa gidan sauki wajen gyaran wayar salula a garin Birnin kebbi.

Post a Comment

 
Top