...Idan Ba Mu Kore Ta Ba A 2019, Wallahi Kana Gida Za A Kwankwasa ma A Sace Ka Don Haka Korar APC Jihadi ne, Cewar Muttaqa Rabe Darma

Daga Jamilu Dabawa, Katsina 

Tsohan shugaban hukumar Kula da asusun man fetur ta kasa wato (PTDF) kuma jigo a jam'iyyar adawa ta PDP a jihar Katsina, Injiniya Muttaqa Rabe Darma ya bayyana cewa babu wani abun da jam'iyyar APC ta amfanawa 'yan Nijeriya sai kawo zaman dar-dar da rashin tsaro da satar mutane da ya ki ci ya ki cinyewa.

Muttaqa Rabe ya bayyana haka ne a hedkwatar jam'iyyar PDP a lokacin da ake kaddamar da shugabannin kungiyar 'Atiku Change The Change' reshen jihar Katsina.

Injiniya Muttaqa ya kara da cewa "sakamakon farfagandar da APC ta yi a can baya shi ya haifar da dukkan wadannan matsaloli da suke ta kara ta'azarra. Akwai lokacin fa da aka sace mutune arba'in da daya a Zamfara, ya fito a wata kafa, ya ce su maido masu shanun su, su maido mana mutanen ku.

"A da, da ni da ku babu wanda ya san satar jama'a har a je a yi cinikin su kamar wasu awaki, jam'iyyar APC ta kawo mana shi. A sace mutum a wannan mulki na APC ya Kai miliyoyin nairori kana a sako shi, wanda ya zama ruwan dare. Dukkan wadannan matsaloli idan ba mu tashi tsaye ba muka Kori jam'iyyar APC ba, kana zaune gidanka barayin mutanen nan za su Kwankwasa ma gida a tafi da kai, sai an saida wannan gida naka a amso ka. Kamar yadda ya fara faruwa a Gachi da ke Karamar hukumar Kankiya".

Muttaqa Rabe ya cigaba da cewa korar APC a kowane mataki jihadi ne, domin magance wannan balai da ta kawo mana a cikin kasa. Yanzu ba yunwa ke akwai ba, abinda ke yunwar nan misali jihar Katsina kudin da ake ba mu da na kasar baki daya ana sanya su ta wata hanyar da bai kamata ba. Saboda hatta majalisar dinkin duniya ta tabbatar da cewa Nijeriya ita ce kasar da tafi kowacce kasa talauci a duniya. Shi kuma talauci yana kawo ta'adanci, yunwa, shiga mata harkar karuwanci, malaman addini su yi karya domin a ba su wani abu, yana sa dan kauye ya shigo birni.

Daga karshe ya yi kira ga 'yan Nijeriya su zabi jam'iyyar PDP a kowane mataki domin fitar da su daga cikin kangin talauci da yunwa da rashin tsaro da APC ta jefa al'ummar kasar nan.

Post a Comment

 
Top