Dan takarar shugabancin kasa na jam'iyyar PDP Atiku Abubakar ya yiwa dukkan ma'aikatan da ke karkashinsa karin albashi zuwa N33,000.
Mohammed El-Yakub, Direktan Gotel Communications, kamfanin sadarwa mallakar Atiku da ke Yola ya tabbatarwa Sahara Reporters a yau Alhamis inda ya ce, "za a fara biyan sabuwar albashin mafi karanci na N33,000 daga watan Nuwamban 2018. Kuma karin albashin ya shafi dukkan wadanda ke aiki karkashin Atiku har da masu hidima a gidajensa."
El-Yakub ya bayyana cewa a halin yanzu akwai kimanin mutane 100,000 da ke karbar albashi a kowanne wata a karkashin tsohon mataimakin shugaban kasar.
Atiku ya yi kira ga shugaba Muhammadu Buhari ya amince da N30,000 a matsayin albashi mafi karanci kamar yadda kwamitin albashi da shugaban kasar ya kafa suka shawarci shi a cikin rahoton da suka gabatar masa.
Post a Comment