Tambaya 1: Wanene kai Jaafar Jaafar a cikin yan jaridun Najeriya.
Amsa: Nine dai Jaafar Jaafar, mai buga jaridar Daily Nigeria.
Tambaya 2: Wacce hukumace ta baka lasisin buga labarai.
Amsa: Nan ya mika masu kwafin takarda da babu wanda yasan me ta kunsa, sai mambobin.
Tambaya 3: Su wanene yan kwangilar da suka shaida maka Gwamna Ganduje na karbar rashawa daga yan kwangila.
Amsa: Baku duba dokokin kasa da suka haramtawa yan jaridu bayyana sunan masu bada labarai garemu.
Tambaya 4: Mu nan ba kasa bace, majalisar jihar Kano ce. Ka fadamana su waye.
Amsa: A’a.
Tambaya 5: Mun san yan kwangilar mu kaf. Tunda muna taka rawa kan ayyukan kwangiloli.
Amsa: Hakan yazo da sauki, sai ku gayyacesu kamar yadda kuka gayyaceni.
Tambaya 6: Ta yaya ka mallaki “video cliffs” (clip) din da kake saki, wa ya tantance maka gaskiyarsu.
Amsa: Na fada maku a baya dokar kasa ta bada kariya ga abinda ake kira ‘source’ wato masu kawo bayanai. Saannan “video cliffs” kamar yadda kuka ambacesu a takardar gayyatata sun zama mallakar kowannenku, kuna iya amfani da kwararru su tantance gaskiyarsu ko akasin haka.
Tambaya 7: Ba zaka fada mana su waye suka baka video da kuma bayarda $5m, jakan zai sanyamu kai ruwa rana da kai.
Amsa: Wadannanne tambayoyinnaku da kuka katsemin aikina, har na baro ofoshina a Abuja. Babu komai dolene mutum irina ya mutunta majalisar dokoki. Kuma kada ku manta, lokacin da na fidda zargin almundahanar kudi a masarautar Kano baku gayyaceni ba, kuka shiga aikin bincike gadan gadan.
Jaafar Jaafar: Nagode muku zan koma kan aikina a can Abuja, sai kun tanadi wasu tambayoyin ko kuma kun gayyaci duk yan kwangilar gwamnatinnan kan ko suna baiwa gwamna Ganduje rashawa.
Tashi-tashi an dawo da wutar ka koma daki. Nan na ankara mafarki nake.
Post a Comment
Click to see the code!
To insert emoticon you must added at least one space before the code.