Rahotanni daga birnin Kaduna na cewa wasu yan bidiga sun sace Basaraken Adara, Maiwada Galadima tare da matarshi yayin da suke cikin tafiya a jerin gwanon motocinsa a kusa da kauyen Maikyali kan hanyar Kaduna zuwa Kachia, a karamar hukumar Kachia na jihar Kaduna.


Wata majiya ta ce yan bindigar sun tare tawagar motocin basaraken ne da misali karfe 6:30 na yamma, kuma nan take suka buda wuta da bindigogi sakamakon haka suka kashe dansanda da ke tare da basaraken tare da wasu mutum hudu. Daga bisani suka tafi da basaraken tare da matarsa.

Kakakin hukumar yansandan jihar Kadna DSP Yakubu Sabo ya tabbatar da faruwar lamarin, ya kuma ce an hada tawaga ta musamman ta soji,yansanda tare da 'yan banga suka bazama a cikin dajin domin bincike.Hakazalika an nemi taimako daga sashen IGP IRT domin samun taimakon fasaha.

Tuni aka kai gawakin wadanda aka kashe Asibitin Kachia

Shiga shafin mu na Facebook facebook.com/isyakuweb Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0 Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

KANA ZAUNE A BIRNIN KEBBI? WAYAR KA TA LALACE KO KANA BUKATAR FLASHING? 

Garzaya zuwa SENIORA TECH,shago mai lamba 50, hawa na sama gefen hagu,TAUSHI PLAZA , yamma daga gidan marigayi Waziri Umaru,kan Tiltin Ahmadu Bello, Nassarawa, Birnin kebbi. Barka da zuwa gidan sauki wajen gyaran wayar salula a garin Birnin kebbi.

Post a Comment

 
Top