Fitaccen Malamin Addinin Musulunci a Nigeria kuma kwamandan rundunar Hisbah ta jihar Kano Sheikh Aminu Daurawa yay magantu akan batun Videon zargin rashawa da ake yiwa Gwamnan Jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje.

A cikin hudubarsa ta Yau Jumu’a a Masallachin sa dake Unguwar Fagge Sheikh Daurawa Ya kalli Lamarin ta kowane bangare nan gida Nigeria dama yadda duniya ta sanya idanu akai.

Ya kuma ja hankalin majalisar jihar Kano kan ta tsaya Kai Da fata wajen tabbatar da gaskiyar lamarin.
Ya kuma musalta Lamarin da kisan Dan Jaridar nan Jamal Kashoggi da akayi a ofishin jakadancin Saudia dake kasar Turkey, kar dai na cikaku da surutu ga cikakken jawabin nasa:

Download Audio  Hudubar Cin Hanci 

Post a Comment

 
Top