Wani labari da muka samu daga jihar Plateau ya tabbatar cewa wasu da ake kyautata zaton cewa matsafa ne sun kwakwale idanun wata mata a gonarta da ke kauyen Kunga a karamar hukumar Jos ta Arewa bayan tsohuwar ta shiga gonarta domin ta samo wa jikokinta abin da za su yi kalaci.

Wani mai suna David Ayuba ya ce tsohuwar ta hadu da wasu mutane guda biyu a kan hanyarta na dawowa daga gonar, kuma suka nemi su taimaketa, amma sai ta ki domin tana tsoronsu.

Ya kara da cewa daga nan ne mutanen suka kamata suka kayar da ita sai suka yi mata allura, tsohuwar ta ce daga nan bata san me ke faruwa ba, domin bayan ta farka daga barci sai ta lura cewa babu idanunta, sakamakon haka bata gani.

Tsohuwar ta yi wa Allah godiya da mutanen su biyu basu kashe ta ba, duk da halin da suka jefa ta na rashin idanu. Yanzu haka tsohuwar tana Asibitin koyarwa na Jami'ar Jos tana karbar magani.

Daga sashenmu na jakar magori

Shiga shafin mu na Facebook facebook.com/isyakuweb Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0 Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

KANA ZAUNE A BIRNIN KEBBI? WAYAR KA TA LALACE KO KANA BUKATAR FLASHING? 

Garzaya zuwa SENIORA TECH,shago mai lamba 50, hawa na sama gefen hagu,TAUSHI PLAZA , yamma daga gidan marigayi Waziri Umaru,kan Tiltin Ahmadu Bello, Nassarawa, Birnin kebbi. Barka da zuwa gidan sauki wajen gyaran wayar salula a garin Birnin kebbi.

Post a Comment

 
Top