Jakar Magori a yau, ta samo mana wani labari mai ban tausayi daga jihar Edo, domin dai hotuna ne aka samo na wata budurwa da aka kasheta kuma aka jefar da gawarta a cikin daji a garin Amagba da ke kan hanyar Sapele a cikin jihar ta Edo.

An ga wani katako da dutse da ake kyautata zaton cewa an yi amfani da su ne aka kashe wannan budurwa.

Bayanai sun ce budurwar ta mutu ta bar diya guda.

Kashe yan mata a jefar a gefen titi ko a jefar a wani kangon gida ya zama ruwan dare a kudancin Najeriya. Abu ne mawuyaci a shafe wata daya ba'a tsinci gawar budurwa ba a mace. Wani abin mamaki shi ne yadda akan yi ma wadannan yanmata zindir kafin a kashe su. Duba da sauraro daga hukumomin jami'an tsaro, da wuya da ji an ambato cewa an kama wadanda ke aikata wannan mugun aiki ga yanmatan.

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0 Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

KANA ZAUNE A BIRNIN KEBBI? WAYAR KA TA LALACE KO KANA BUKATAR FLASHING? 

Garzaya zuwa SENIORA TECH,shago mai lamba 50, hawa na sama gefen hagu,TAUSHI PLAZA , yamma daga gidan marigayi Waziri Umaru,kan Tiltin Ahmadu Bello, Nassarawa, Birnin kebbi. Barka da zuwa gidan sauki wajen gyaran wayar salula a garin Birnin kebbi.

Post a Comment

 
Top