An gurfanar da wani tsohon biri mai suna Abdullahi Sani dan shekara 50 a gaban wata Kotun Majistare a garin Funtua na jihar Katsina ,bayan an zarge shi da taushe diyar makwabcinsa yar shekara uku kuma ya yi lalata da ita har ta mutu.

Sani ya lallabi yarinyar ce zuwa wani kangon gida inda ya yi mata fyade. Domin ya hana ta yin ihu saboda neman agaji, Sani ya yi amfani da hannunsa ya toshe bakin yarinyar sakamakon shakewa domin rashin iska, sai yarinyar ta mutu, kamar yadda dansanda mai gabatar da kara ya shaida wa Kotu.

Alkalin Kotun Hajiya Fadile Dikko, ta dage sauraron karar har zuwa ranar 20 ga watan Nuwamba 2018, kuma ta tasa keyar Sani zuwa Kurkuku kafin wannan ranar.

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0 Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

KANA ZAUNE A BIRNIN KEBBI? WAYAR KA TA LALACE KO KANA BUKATAR FLASHING? 

Garzaya zuwa SENIORA TECH,shago mai lamba 50, hawa na sama gefen hagu,TAUSHI PLAZA , yamma daga gidan marigayi Waziri Umaru,kan Tiltin Ahmadu Bello, Nassarawa, Birnin kebbi. Barka da zuwa gidan sauki wajen gyaran wayar salula a garin Birnin kebbi.

Post a Comment

 
Top