Jakar Magori na shifin isyaku.com, ya leko mana jihar Anambra, inda ya samo hotuna tare da labarin yadda al'ummar kauyen Etitnabo Ezihu da ke garin Igboukwu suka kama wasu yan fashi, kuma suka yi masu zindir, har da tukuicin wulakanci.Wadannan 'yan fashi sun shiga wani wajen bauta na gargajiya, inda suka yi kokarin sace wasu ababen bauta tare da wasu keke-kere na gargajiya masu daraja a kasuwa.Amma daga bisani sai dubunsu ta cika yayin da suke kokarin tserewa.

Sakamakon haka ne ya sa 'yan fashin suka fara harbin mai uwa da wabi, amma Allah ya kiyaye domin dai babu wanda harsashi ya sameshi, jama'a sun ranta na kare suka sami mafaka. Amma fa daga bisani, kauyawan dai sun yi nassarar damke wadannan yan fashi bayan sun yi atisayen gudun fitar rai domin neman tsira, amma fa suka kasa saboda matasa sun kama su a hannu.

Nan ne fa 'yan fashi suka gamu da fushin fusatattun samari da suka lafta masu dan karen duka, suka tube su zindir, suka jagwalgwala su iya yadda suka bukata, bayan wannan tozarci, sai aka mika su ga 'yansanda domin su fuskanci tuhuma.

Ka ji yadda ta kasance da katta marasa godiya ga Allah da ya basu koshin lafiya

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0 Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

KANA ZAUNE A BIRNIN KEBBI? WAYAR KA TA LALACE KO KANA BUKATAR FLASHING? 

Garzaya zuwa SENIORA TECH,shago mai lamba 50, hawa na sama gefen hagu,TAUSHI PLAZA , yamma daga gidan marigayi Waziri Umaru,kan Tiltin Ahmadu Bello, Nassarawa, Birnin kebbi. Barka da zuwa gidan sauki wajen gyaran wayar salula a garin Birnin kebbi.

Post a Comment

 
Top