Rahotanni daga garin Kolomo da ke gundumar kudancin kasar Zambia sun ce,da sanyin safiyar yau, wasu bata gari sun jefa wani mutum kan taragon hanyar jirgin kasa, sakamakon haka jirgin ya bi ta kafafunsa kuma suka gundule.

Rahotanni sun ce rigima ce ta kaure tsakaninsa da wasu mutane bisa lamarin bashi da ya shafi Massara da wanda lamarin ya faru da shi  mai suna Mubita Sianzuki ya kasa biya. Sakamakon haka mutanen suka aikata masa wannan danyen aiki.

Amma wata majiya ta ce , mutanen, sun yi amfani da adda ne suka sassare masa kafafunsa, kafin suka dauko shi suka sa shi a hanyar taragon jirgin kasa domin a yi tunani cewa jirgi ne ya bi ta kafafunsa.

Hakazalika, bayanai sun tabbatar cewa yanzu haka yansanda sun fara gudanar da bincike akan lamarin.

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0 Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

KANA ZAUNE A BIRNIN KEBBI? WAYAR KA TA LALACE KO KANA BUKATAR FLASHING?

Garzaya zuwa SENIORA TECH,shago mai lamba 50, hawa na sama gefen hagu,TAUSHI PLAZA , yamma daga gidan marigayi Waziri Umaru,kan Tiltin Ahmadu Bello, Nassarawa, Birnin kebbi. Barka da zuwa gidan sauki wajen gyaran wayar salula a garin Birnin kebbi.

Post a Comment

 
Top