Shugaban jam'iyyar APC na kasa Bola Ahmed Tinibu ya ziyarci Mazaba ta C da ke unguwar Alausa da birnin Ikko, wataU Lagos, domin ba magoya bayan jam'iyyar APC kwarin guiwa a zaben fidda gwani na Gwamnan jihar Lagos da ake gudanarwa. Amma fa bayan Tinibu ya bar wajen, sai rigima ya kaure, domin wasu sun sha mari, wasu kuma suka sha Kung Fu daga gwanannu, wasu kuma suka sha zagi, lamarin ya faru ne bayan an yi zargin cewa Tinibu ya ba Matasan Alausa wasu kudade da ba'a fayyace ko nawa ne ba. Sakamakon haka yanayi ya canja, domin fa kowa ta kanshi ya yi domin ganin ya sami nashi rabo.

Yanzu dai, bayanai suna nuna cewa dan takara da Bola Tinibu ke mara wa baya Babajide Sanwo-Olu, shi ne ya lashe sakamakon zabe na Mazaba ta C da ke Alausa.

Jami'in zabe da ke kula da Mazabar C na Alausa,  Olanrewaju Yahaya, ya sanar da sakamakon zaben na Mazaba ta C, Alausa. Ya ce Sanwo-Olu yana da kuri'u 960 yayin da Gwamna Ambode ke da kuri'u hudu kacal a wannan Mazaba.

Dangantaka dai ta yi tsami tsakanin Tinubu da Ambode gabanin zaben fidda gwani wanda zai tsaya takarar kujerar Gwamnan jihar Lagos karkashin jam'iyyar APC.

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0 Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira KANA ZAUNE A BIRNIN KEBBI? WAYAR KA TA LALACE KO KANA BUKATAR FLASHING? Garzaya zuwa SENIORA TECH,shago mai lamba 50,hawa na sama gefen hagu,TAUSHI PLAZA , yamma daga gidan marigayi Waziri Umaru,kan Tiltin Ahmadu Bello, Nassarawa, Birnin kebbi. Barka da zuwa gida sauki wajen gyaran wayar salula a garin Birnin kebbi

Post a Comment

 
Top