Yan bindiga sun halaka mutune goma sha tara a kauyen Ariri da ke karamar hukumar Bassa a jihar Plateau ranar Laraba. Rahoto ya nuna cewa maharan sun kai hari ne da talatainin dare kuma suka harbe mutanen yayin da suke barci.

Makwabata sun ce jami'an tsaro basu iso wajen ba kafin lokacin daukar hoton lamarin, kuma gawakin na warwatse a haraban gidajen da lamarin ya faru.

A bangare daya kuma, bayanai sun ce akalla mutum 14 ne 'yan kabilar Berom aka kashe ranar Talata da dare a wani hari da aka kai a kauyen Jol da ke karamar hukumar Riyom a cikin jihar Plateau.

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0 Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

KANA ZAUNE A BIRNIN KEBBI? WAYAR KA TA LALACE KO KANA BUKATAR FLASHING? 

Garzaya zuwa SENIORA TECH,shago mai lamba 50, hawa na sama gefen hagu,TAUSHI PLAZA , yamma daga gidan marigayi Waziri Umaru,kan Tiltin Ahmadu Bello, Nassarawa, Birnin kebbi. Barka da zuwa gidan sauki wajen gyaran wayar salula a garin Birnin kebbi.

Post a Comment

 
Top