Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ranar Litinin 1 Ga Oktoba, ta zama ranar hutun murnar zagayowar Ranar ‘yancin Najeriya.


A ranar Litinin 1 Ga Oktoba ne Najeriya za ta cika shekaru 58 da samun ‘yanci.

Ministan Harkokin Cikin Gida, Abdulrahman Dambazau ne ya bayyana haka a cikin wani jawabi da Babban Sakataren Ma’aikatar, Mohammed Umar ya sa wa hannu jiya Alhamis, a Abuja.

Dambazau ya taya ‘yan Najeriya murnar zagayowar ranar, tare da yin kira a ci gaba da jibintar kokarin Gwamnatin Muhammadu wajen wanzar da zaman lafiya a kasar nan, tare da hadin kai a tsakanin juna.

Ministan ya kara da cewa a cikin shekaru 58 da suka shude, Najeriya ta samu gagarimin ci gaba, ba wai a rayuwar al’umma kadai ba, har ma fannin samar da ababen more rayuwar jama’a da kuma karin samun tasiri a kasashen ketare, ta hanyar inganta dangantakar diflomasiyya da kasahen waje.
Premiumtimeshausa.
29 Sep 2018

Post a Comment

Emoticon
:) :)) ;(( :-) =)) ;( ;-( :d :-d @-) :p :o :>) (o) [-( :-? (p) :-s (m) 8-) :-t :-b b-( :-# =p~ $-) (b) (f) x-) (k) (h) (c) cheer
Click to see the code!
To insert emoticon you must added at least one space before the code.

 
Top