Wannan shine kusan duk abin da Sheikh Dr. Ahmad Abubakar Mahmud Gumi ya fada jiya Alhamis 15/11/2018 game da kadiyar kudin rashawa da aka kama gwamnan Kano Ahaji Abdullahi Umar Ganduje.

Malam ya nuna banbanci dake tsakanin kudin da gwamnoni suke canzawa daga wani aiki zuwa wani aiki da kuma karkatar da dukiyar al'umma da cinye ta da suke yi da banbanci tsakanin wanda zai karbi kudi domin ya bada wata kwangila.

Idan kana kare musulunci ne to ka bi abinda musulunci yace, idan kuwa kana kare siyasa ne to ka sani siyasar zata barka a duniya addini ya raka ka lahirarka.

Allah Ya kara tsare mana imanin mu, ya tsare shi kanshi malam.

Salisu Hassan Webmaster
08038892030
16/11/2018

Post a Comment

 
Top