Dan wasan Super eagles zaiyi ma kungiyar mahaifar sa goma ta arziki idan suka zura kwallo a ragar Kano pillars

Yace a ko wani kwallo da tawagar ta zura a ragar abokan adawar su kuma suka yi nasara a wasan kungiyar zata samu naira dubu dari daya.


Mai tsaron bayan ragar tawagar super eagles ta Nijeriya Shehu Abdullahi yace a shirye yake domin yi ma kungiyar mahaifar sa wato Sokoto united goma ta arziki na ko wani kwallo da suka zura a ragar Kano Pillars wasan tare na gasar Aiteo Cup.

A sakon faifan bidiyo da ya wallafa a shafin sa na Tuwita dan wasan yana mara ma kungiyar Sokoto United baya kuma yana karfafa gwiwar su wajen samun galaba.

Yace a ko wani kwallo da tawagar ta zura a ragar abokan adawar su kuma suka yi nasara a wasan kungiyar zata samu naira dubu dari daya.

Dan wasan ya fara wasa a kungiyar Sokoto United da Kano Pillars gabanin zuwan sa kungiyar kasar waje.

Tsohon kungiyoyin sa zasu fafata a rukuni na biyu na gasar kofin Nijeriya ranar lahadi 16 ga watan Satumba.

Ga yadda sauran wasannin rukuni na biyu na gasar zata kaya;

Mighty jets vs Kwara utd

Osun utd vs Katsina utd

Ifeanyi ubah vs J. Atete

Elkanemi Warr vs Katsina utd feeders

Wikki Tourists vs Bayelsa utd

Cofine FC vs Sunshine stars

Crown FC vs Abia Warriors

Kogi utd vs Niger Tornadoes

Nasarawa utd vs Standard FC

Remo stars jnr vs Rivers utd

Yobe stars Plateau utd

Go round vs supreme court

Kebbi Utd vs Enugu Rangers

Post a Comment

 
Top