Tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo ya yi kira ga ƴan Najeriya da su hada hannu wajen yaƙar matsalar rashin tsaro da mulkin son rai a ƙasar nan, Obasanjo ya faɗi hakan ne a wajen bikin cikar Farfesa Ango Abdullahi tsohon mataimakin shugaban jami’ar Ahmadu Bello da ke Zaraiya shekaru 80 da haihuwa wanda aka gudanar ya tilas ne matsalar rashin tsaro a ƙasar nan ke ƙara tabarbarewa.

Kuma Obasanjo ya ce sam bai kamata dattawan ƙasar nan su zura ido akan abin da ke faruwa a halin yanzun ba, yin hakan daidai yake da shuka matsalar wargajewar ƙasar nan, Ba wanda ya isa ya ji cewa zai iya mallakan ƙasar nan a rigimance, matukar kuwa aka kai mutum bango a irin hakan matukar ƙasar mu ba a daidai take tafiya ba, to kuwa ya hau kanku, ƴaƴan mu, matasa da mu iyayenku ba maganan shekaru a nan, da mu hada hannu mu yi aiki tare wajen mayar da ƙasar mu a kan hanya madaidaiciya ba wanda ya isa ya ce, kasata ce ni kadai, don haka zan yi duk yanda na so, Allah ba zai bari hakan ya faru ba.

25 Dec 2018

Post a Comment

Emoticon
:) :)) ;(( :-) =)) ;( ;-( :d :-d @-) :p :o :>) (o) [-( :-? (p) :-s (m) 8-) :-t :-b b-( :-# =p~ $-) (b) (f) x-) (k) (h) (c) cheer
Click to see the code!
To insert emoticon you must added at least one space before the code.

 
Top