Wani tsohon biri dan shekara 64 mai suna  Mr. Joseph Ebowomen ya fada hannun yansanda a birnin Lagos bayan asirinsa ya tuna cewa ya shafe shekara 2 yana lalata da diyar da ya haiafa., Lamarin ya faru ne a Kilometer 47 wanda ke unguwar Titin Lekki da ke Ajah a jihar ta Lagos.

Wannan tsoho ya lalata diyar cikinsa tun 2016, kuma tun wannan lokaci ya mayar da ita budurwarsa karfi da yaji wajen da yake aikata lalata da ita ba tare da son ranta ba.

Ita diyar ce ta tona wa mahaifin nata asiri da kanta, bayan ta kasa jure irin bakinciki da take fuskanta sakamakon yadda ya aikata mata fyade kuma ya mayar da ita wajen kwance sha'awarsa a ko da yaushe.

Tuni dai yansanda suka yi awon gaba da shi kuma suka gurfanar da shi a gaban wata Kotu duk da cewa ya ce Shedan ne ya rude shi kuma ya aikata wannan aiki, daga bisani ya roki gafara kuma ya roka a yafe masa.

Duk da haka , Alkalin Kotun Majistare Magistrate, Mr. Peter Nwaka ya garkame wanda ake kara a Kurkuku har zaman Kotu na gaba.

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0 Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Post a Comment

 
Top